This site uses cookies.
Some of these cookies are essential to the operation of the site,
while others help to improve your experience by providing insights into how the site is being used.
For more information, please see the ProZ.com privacy policy.
This person has a SecurePRO™ card. Because this person is not a ProZ.com Plus subscriber, to view his or her SecurePRO™ card you must be a ProZ.com Business member or Plus subscriber.
Affiliations
This person is not affiliated with any business or Blue Board record at ProZ.com.
English to Hausa - Rates: 0.04 - 0.05 USD per word / 15 - 20 USD per hour Hausa to English - Rates: 0.04 - 0.05 USD per word / 15 - 20 USD per hour Hausa - Rates: 0.04 - 0.05 USD per word / 15 - 20 USD per hour English - Rates: 0.04 - 0.05 USD per word / 15 - 20 USD per hour Arabic to Hausa - Rates: 0.04 - 0.05 USD per word / 15 - 20 USD per hour
Arabic to English - Rates: 0.04 - 0.05 USD per word / 15 - 20 USD per hour Hausa to Arabic - Rates: 0.04 - 0.05 USD per word / 15 - 20 USD per hour English to Arabic - Rates: 0.04 - 0.05 USD per word / 15 - 20 USD per hour
More
Less
Portfolio
Sample translations submitted: 1
English to Hausa: MAGANIN RASHIN SANI. General field: Other
Source text - English MAGANIN RASHIN SANI
WRITTEN BY: MUIDEEN O. JIMOH
CHARACTERS (REGULARS)
DR SEYI: A young dentist posted to Ungwar Dawaki to serve at the primary health care center as a corp member. He has just finished his Residency program from the Aminu Kano teaching hospital.
MAI ANGUWA- The district head of Ungwar Dawaki, an uneducated man in his late fifties.
HAJIYA MAIMUNA: Mai Anguwa’s wife; has a food stall in the market around the motor park
DR BALA-: A dental assistant whose job is to assist the dentist at the primary health center, but parades himself as an all-rounder. He connives with nurse Talatu to scam the community. If he is not at the center, he is extracting tooth in a shop that also doubles as chemist. He has no formal training but has a funny accent when he speaks English and claims to have studied in America
FATIMA- The Mai Anguwa’s only daughter, she is studying Pharmacy in a university in the city, comes home regularly to assist her mother. She is in a relationship with Dr Bala.
NURSE RAMATU- She supposedly “learnt” nursing at some clinic in the city. She and Dr Bala takes care of patients that come to the Primary health center in the village which has been without a doctor, save for corp members posted there once a while. They double as doctor and nurse.
YA’U MAI MAGANI – Primarily, he hawks stimulants and cough syrups to the area boys but also claims to have medicine for every illness. He buys drugs from Dr Bala. They are usually expired before he sells.
IDI: A regular customer of Yau Mai magani and a tricycle rider. He abuses drugs
AUDU- Decent guy, friends with Idi by virtue of being a tricycle operator
HAJIYA SARATU A no nonsense woman and the younger sister to the Mai Anguwa, she visits the Mai Anguwa from time to time
MAMAN AMINA: Idi’s wife; washes plate and run errands for the Mai Anguwa’s wife at her food stall in the market.
EPISODE ONE
ACT ONE. SCENE ONE: LOCATION. EXTERIOR (MORNING)
IN FRONT OF THE PRIMARY HEALTH CARE CENTER, THERE ARE TWO QUEUES, ONE FOR WOMEN AND THE OTHER FOR MEN, THEY ARE ALL WAITING FOR NURSE TALATU, WHO ATTENDS TO THEIR COMPLAINTS, DIAGNOSES AND PRESCRIBES MEDICINE FOR THEM EVERY MONDAY, WEDNESDAY AND FRIDAYS.
SOUND: SOMEONE CAN BE HEARD COUGHING IN THE BACKGROUND
MAN 1: (TO MAN 2) Will this Nurse even show up today kuwa, haba dan Allah, some of us have been here since 6.30 am
And uptil now she hasn’t come, later now they will say the government isn’t working, when ordinary people like nurses don’t even come to work early, look it’s almost 9.00 am.
MAN2: Wallahi kuwa, if not that the city is far, I would have Just gone to asibitin Murtala kawai. And they have stopped bringing corp members to our community, since the last one left two years ago.
So, Mallam (TALKING TO MAN 1) what is wrong with you ne wai.
MAN 1: Wallahi Mallam, it is my gum, it has been swollen for days now, and I have been using a chewing stick I bought at the market hoping it would cure it, amma uptil now walahi, no improvement. So I decided to come meet nurse Ramatu to give me some medicine for it.
MAN2: Wai, ikon Allah, I had a similar experience a month Back, Dr Bala gave me some medicine and the pain went away after a few days, but when it came back, it got worse, Allah ne ya so ni wallahi…
SOUND: APPROACHING TRICYCLE
(IT IS 9.00 AND THE NURSE WALKS IN CARRYING A BAG).
NURSE RAMATU: Good morning everyone, An tashi lafiya, sorry I am late. My brother isn’t feeling too well, so I took him to the hospital in town, I am just coming back. He has been admitted.
WOMAN 1: Ayyah, Allah ya bashi lafiya, sannu da zuwa nurse.
HAJIYA SARATU: (SARCASTICALLY) Amma Nurse, what is really
wrong with him that is beyond you to treat here that you had to take him to the city?
I thought you said there is no ailment you and Dr Bala could not treat. Ashe duk bulla ne! duk papa ne!
SOUND: NURSE HISSING, KEY TURNS IN LOCK, DOOR OPENS AND SHUTS
SCENE TWO: ACT ONE.LOCATION.INT (MORNING)
(THE NURSE SITS IN FRONT OF MAN 1 IN WHAT IS A MAKESHIFT CONSULTING ROOM). NURSE RAMATU: So, what is wrong with you Mallam?
MAN 1: Nurse, last week, I just felt some pain in my gums while using charcoal to clean my mouth, so after a few days and the pain didn’t go away, I went to the market to buy aswaki. But a few days after I started using the chewing stick, I noticed the gums were swollen and I bled most times, infact I am bleeding now.
NURSE RAMATU: Okay, open your mouth?
(IRRITATED)
Wai wai wai. Mallam this teeth has expired walahi.
You need to go to Dr Bala to get them removed.
Neeeeeeext!
MAN1: Wait nurse, ban gane ba? na je na cire hakori na?
Lalle, baban Magana. Isn’t there some medicine you can at least give me for the pain please?
NURSE RAMATU: Wallahi no, just go to Dr Bala. He is an expert in
removing teeth. Dubu daya ne kawai. Don Allah ka fita ka ba sauran mutanen dama su shigo.
SOUND: SCREECH OF A CHAIR IS HEARD AS MAN 1 MAKES HIS EXIT, HE BANGS THE DOOR ANGRILY BEHIND HIM, SHORTLY AFTER, WOMAN 2 ENTERS.
NURSE RAMATU: Welcome please, what’s wrong with you?
(SHE LOOKS UP AND REALIZES IT WAS THE WOMAN WHO MOCKED HER FOR TAKING HER
BROTHER TO THE CITY HOSPITAL)
Neeeeeeexxxxxxxt
HAJIYA SARATU:
SOUND: SEAT SHUFFLING Ahn ahn Nurse, but you haven’t even attended to me and you are already calling next. Ah, please o
I am not feeling very fine Nurse……
NURSE RAMATU: So what do you want me to do about it?
(TURNS ON THE TRANSISTOR RADIO ON HER TABLE TO A HIGH PITCH, COMPLETELY IGNORING THE PATIENT IN FRONT OF HER
AND INTERRUPTING HER COMPLAINS)
SOUND: RADIO BLARING LOUDLY
(HOT ON MIKE)
Look woman, I don’t have time to listen to anything you have to say, for all I care, whatever is wrong with you can as well kill you.
HAJIYA SARATU: Ah! Nurse, have I offended you before now? What
could I have possibly done to you? Ikon Allah
NURSE RAMATU: oh oh oh oh,
What could you have possibly done to me abi?
(TURNS DOWN THE VOLUME OF THE RADIO.)
So, you come here and laugh at me, insulting me for taking my brother to the hospital in the city? Since I am not capable of attending to your needs here, so why are you here, you can as well leave. Shikenan Neeeeeeeeexxxxxt!
HAJIYA SARATU: (CURSING LOUDLY AND TRYING TO GET INTO A SCUFFLE WITH THE NURSE)
Allah ya isa, maiya. I will expose your secret to the whole community; you are a scam, a fake nurse,
Uhuhuhuhuhuhuhuhuhuhuhu, if you knew you were capable, why did you take your brother to the city?
Look, woman, the Mai Anguwa must hear this. I know all your secrets. Let me just go and come back into this community, I will have your time. Witch.
NURSE RAMATU: Neeeeeeeeext!
(NURSE RAMATU SHOVES HAJIYA SARATU
THROUGH THE EXIT AND CALLS THE NEXT PATIENT IN)
SOUND: DOOR BANGS LOUDLY
MAN 2: Good Morning Nurse Ramatu.
NURSE RAMATU: Good morning, so, you kuma what is wrong with you this time?
MAN 2: I had this small cut a few days ago on my leg, I put some kerosene to stop the blood and thereafter applied the juice from dogon yaro leaves and some cow dung, but after a while, it started bringing out pus and some terrible smell. And the pain has doubled too.
NURSE RAMATU kai kai kai kai, inalillah wa ina ilaehi rajiun. Ai Mallam, bilahi lazi this leg has expired, sai dai a yanka ta a sa maka na roba.
Fita kaba saura wuri. Please go out and let others come in.
Neeeeeeeeeeeeeeext!.
MAN 2: Inalillahi wa ina ilaehi rajiun, inalillahi wa ina ilaehi rajiun, nurse shikenan sai an yanke mun kafa?
Nurse don Allah, please help me, don’t tell me nothing else can be done, please.
SOUND: MAN 2 CRYING
NURSE RAMATU: (MONOLOGUE) Mmmscheewww, sha sha sha, if people ask them to
Come to the clinic for proper medication, they will not come; now his leg is ruptured and there is nothing I can do for him.
Wai, who is the next person ne wai?
Neeeeeeeeext!
SOUND: BABY CRYING AS DOOR OPENS AND CLOSES
MAMAN AMINA: Ina kwana Nurse Ramatu.
NURSE RAMATU: Antashi lafiya? What’s wrong with your baby?
MAMAN AMINA: I don’t know for sure, but I notice that it seems she
wants to grow her first set of teeth; they are sprouting already, so she has had some fever for days now.
NURSE RAMATU: Ayyah, sorry baby.
MAMAN AMINA: She doesn’t sleep at night, she is often restless and her body gets very hot at intervals. Please help us.
NURSE RAMATU: kai, kuma gashi I don’t have the teething injection here, dana ba ta. But here is what you should do, I will write some medicine for you, go to the chemist down the street on your way to the market, he is
always there, tell him to give you paracetamol, folic acid, and ibuprofen, and if he doesn’t have, buy from the young man that hawks medicine around the market. Ko a ina kike so, ki dei siya ki bata da wuri wuri
Give them to your baby, she will be fine in no time.
Neeeeeeext person!
MAMAN AMINA: Ah, Nurse but all these are tablets now, this girl is barely a year old, I was thinking you would give her some syrup, you even mentioned injection, for teething?
NURSE RAMATU: Look woman, I don’t have time for this rubbish, if
you will not go and buy the drugs, whatever happens to your child, baa ruwana.
Wait do you think I don’t know what I am doing? I spent ten years training for this job, tell me again, how many years do Medical doctors actually spend in medical school, I am over qualified let me tell you. Infact, leave my office, you and your baby are expired!
SOUND: MUSIC
THE END
EPISODE TWO
ACT ONE. SCENE ONE. LOCATION: INTERIOR (AFTERNOON)
(DR BALA SITS INSIDE A SHOP WHERE HE SELLS MEDICINE AND PERFORMS TOOTH EXTRACTION AND CLAIMS TO TREAT ALL MANNER OF ILLNESSES).
MAN 1: Good morning Dr Bala.
DR BALA: Good Morning Mallam, yaa iyali? What can I do for you this morning?
MAN 1: Wallahi Likita, I have been to the health center and didn’t meet you, and you know since the government stopped deploying corp members to the clinic, we have been at the mercy of you and Nurse Ramatu.
DR BALA: Actually, this is a profound statement and very true in every ramification. You see as a concerned citizen of this community, it is important to contribute our quota to preserving the health of the citizenry. That’s why we are here, what the government doesn’t know is that, you cannot compare a man who studied in America to a man who schooled in Kano, Haba Mallam, akwai banbanci fa!
MAN 1: Haka ne Likita, toh Likita walahi this my tooth is giving me problems, after the chewing stick I bought at the market the last time, it has gotten worse, so I went to see Nurse Ramatu at the clinic and she said nothing else can be done except we extract the bad tooth.
DR BALA: Come close, let me take a look
SOUND: FEET SHUFFLING AS MAN 1 MOVES CLOSER TO THE DR
DR BALA: la la la la, wai. Hold it right there Mallam, wai
wannan warin, daga bakin ka ne haka. Magana ya lalace wallahi.
We have to remove the bad teeth with immediate
alacrity.
MAN 1: kai, inalillahi, isn’t there anything you can do for me other than remove the teeth likita?
DR BALA: Mallam, bilahilazi ko an kaika Amrika, these teeth have to go.
MAN 1: Inalillahi wa ina ilaehi rajiun, toh yanzu Dr Bala how much will the extraction cost me?
DR BALA: Dubu daya ne cire hakori guda daya, kuma naga guda uku ne basu da kyau, ka ga ya kama dubu uku kenan, ga dubu daya kudin ganin likita, ga dari biyar kudin form, ga wata dubu uku kudin maganin da zan baka. Kaga duka gaba daya ya kama dubu bakwai da dari biyar kacal.
MAN 1: Subhanallah, haba Dr, kudin nan yayi yawa fa, where will I get that kind of money now cikin wannnan yanayin?
DR BALA: toh shikenan, sai ka tafi ka ban wuri, yanzu ba uku bane su ka lalace, bayan sati biyu, duk bakin ka zai gama rube wa, zaka gane. Dariya a waje ma zai maka wahala.
MAN 1: Toh shikenan likita, zan biya, a zo a cire. Ga dubu bakwai, su kenan, don Allah a yi hakuri haka.
DR BALA: (EXCITEDLY) Shikenan, kwanta, ga benci nan bayan ka.
MAN 1: (WHISPERS)Ya Allah ga bawon ka a hannun ka, ka taimaka mani.
DR BALA: Yau Mallam, ni ne mai taimaka maka.
SOUND: METAL TOOLS; A HAMMER, CHISEL AND PLIER CLANG
MAN 1: wait, wait, wait likita, who do you intend to tie with this large rope? Haba, when I am not a cow.
DR BALA: Walahi, kai din ne, ka natsu mugama abin nan sharp sharp.
MAN 1: Wai Likita, tsaya,tukun mana, I see you with a
hammer, plier and chisel, are you about to crush some rocks?
SOUND: SCUFFLE BETWEEN DR BALA AND MAN 1 AS THE DR FORCEFULLY TIES HIM TO CARRY OUT THE EXTRACTION. THIS SOUND IS HEARD TILL FADE
ACT ONE. SCENE TWO. LOCATION: EXTERIOR (AFTERNOON)
SOUND: VOICES ARE HEARD AS PEOPLE COME AND GO IN FRONT OF DR BALA’S
SHOP (MAN 2 APPROACHES DR BALA).
MAN 2: Good afternoon Dr Bala, yaa iyali, yaa aiki kuma?
DR BALA: lafiya kalau Mallam, yaa yau. Barka da shigo wa, kai kai kai, mei ya sami kafan ka haka, na ga har tsutsa yake fitowa a ciki, inalillah. Kai amma kafan nan ya rube.
MAN 2: (IN A SAD VOICE) Walahi likita, daga wurin nurse Ramatu na ke, ta ce na zo na same ka, wai baa bin yi, sai dei a yanke ta kawai.
Inalillah wa ina ilaehi rajiun.
DR BALA: let’s just go in so I can amputate the leg quickly before it affects the other one, you know this thing spreads easily and quickly too.
SOUND: DOOR OPENS AS BOTH MEN ENTER INTO THE SHOP
MAN 2: Inalilahi wa ina ilaehi rajiun, so how much will it cost to amputate the leg doctor?
DR BALA: dubu ashirin kawai ne, ga kuma kudin magani dubu biyar, kudin ganin likita dubu daya, kudin form dari biyar kaga dubu ashirin da shida da dari biyar ke nan.
MAN 2: inalillah, Ya Allah ka taimake ni, gaa kudin likita.
DR BALA: (COUNTS THE MONEY), daya, biyu, uku…
Ashirin da hudu, ashirin da biyar, ashirin da shida..
Yawwa, sun cika, deidei.
Toh, ga benci nan bayan ka, kwanta.
SOUND: SCUFFLE AS A STRUGGLE ENSUES BETWEEN THE DR AND MAN 1
MAN 1: Waaayo Allah, waaayoooo, na mutu, waaayoo
DR BALA: Hold still please, this will only take five minutes and we will be done.
MAN 1: Wait, please I don’t understand, you want to chop off my legs and you won’t give me something first for the pain? What kind of Dr are you please? Please give me my money. I am not interested in this procedure again.
Haba!
DR BALA: It’s not even going to hurt, you will only feel a little pinch as the saw goes through your bones, sharp sharp and we are done.
MAN 1: Ah, no thank you, I think you should simply stick to removing teeth and not chopping off limbs, now please pass me my money.
DR BALA: You know Hamisu Gurgu? I was the one that chopped off his leg when he got cancer in there?
Even Maman Sale from the next village, I chopped off one of her hands too, I have been doing this for ages. Don’t worry.
MAN 1: Yes, I know them both, and I also know that they both died a few weeks after you chopped off their limbs. Hmmn, so the rumors about you are true. You will meet your nemesis very soon, you this quack doctor and evil man.
DR BALA: please, please, don’t you dare insult me, I am a chief surgeon and professional, I trained in America and I have worked at different teaching hospitals, don’t come here and try to teach me my job, I will not take it, now take your useless money and rotten leg out of my clinic.
MAN 1: you call this place a clinic? Mscchew
SOUND: DOOR SLAMS AFTER MAN 1 PICKS UP HIS MONEY AND LEAVES
DR BALA: (HOT ON MIKE) Useless man, he wants to ruin a day which has already started well for me, Allah ya issa, kai, see the way I just missed a cool 26,500 naira fa.
Kai, kai, kai. Amma gayen nan, dan iska ne!
SOUND: THEME SONG PLAYS TILL FADE
ACT TWO. SCENE ONE: LOCATION.INT. (EVENING)
(NURSE RAMATU IS SITTING INSIDE DR BALA’S SHOP, TOGETHER THEY
DISCUSS THE DAY’S BUSINESS)
NURSE RAMATU: So that guy with the rotten teeth and bad breadth came to get his teeth extracted ko?
Nina turo shi ai, I told him you were his last bustop.
DR BALA (LAUGHS) walahi, three of his teeth had to go, they were so bad already, and he was busy screaming like a baby.
NURSE RAMATU: kace yau kayi kasuwa kenan?
DR BALA: Gaskiya ba laifi, mun gode wa Allah, yaa health center din? I will be around tomorrow in shaa Allah
NURSE RAMATU Dr Bala, don Allah ka san abin da ya kawo ni, salame ni na kama gaba.
DR BALA: ehhehehe, Nurse Nurse kenan, ai na sani, toh kin dai ga yau sai a hankali, hakori kawai na cire, kuma dubu uku ne na karba. Toh gashi, ga dubu daya. Na gode.
NURSE RAMATU: kai Mallam, kar ma ka raina min hankali, yaushe ka fara karya?
DR BALA: Haba Nurse, Karya kuma? Walahi shikenan abin da na yi tun safe.
NURSE RAMATU: What about the guy for amputation that I sent over? Please don’t play games with me.
DR BALA: Ah, that one, that one was an overdose of bad market o, do you believe he had even paid, but when he saw the sharp edge of my saw, he just freaked out saying something about giving him medicine for the pain he will feel. Obviously he had heard some news about me and decided he no longer wanted the surgery. I just gave him his money back, you see those kind of people, fear them, they can take you out of business.
NURSE RAMATU: Haba, toh, oya pass me my commission please, I have to be in town now, my brother Mukhtar has been sick, and He is on admission at the city Hospital. I need to go be with him.
DR BALA: Haba, mei ya same shi?
NURSE RAMATU: Zazabi ne da ciwon kafa, kawai ya kasa tafiya sosai.
DR BALA: Ah, Nurse Ramatu, this simply means that his leg has expired ooo, and he needs to come for amputation before it spreads to the hands. Please just go and bring him so I can perform the surgery on him sharp sharp
NURSE RAMATU: Allah ya kiyaye, kafin ka ne yayi expire!
SOUND: MUSIC TILL FADE
THE END
EPISODE THREE ACT ONE. SCENE ONE. LOCATION: EXTERIOR (MORNING) SOUND: THE HUSTLE AND BUSTLE OF A MARKET SCENE.
YA’U MAI MAGANI: A siya magani, ciwon kai, ciwon baya, ciwon kafa, ciwon ido, ciwon kirji, ciwon mara, a siya magani.
Akwai na kanjamau, na daji, na kwantartar ciki ma a kwai, a siya magani.
Alhaji a miko ma na bassir ne?
SOUND: THE ROAR OF A TRICYCLE Hajiya naga idon kin na ruwa ruwa, a kawo maki eye tablets ne?
IDI: Kai Ya’u, yaane?
YA’U MAI MAGANI: Gwaska Idi, lafiya, yaa aiki
IDI: yaa dei, hado min as usual mana.
YA’U MAI MAGANI: an gama, gwaska, na dari bakwai ko?
IDI: yau sai a slow, hado na dari biyar kawai, naga yaa ne, kaga ne ai
YAU MAI MAGANI: ba komai gwaska, an hado, ga shinan.
SOUND: MONEY AND DRUG EXCHANGE HANDS, THEN THE REV OF THE BIKE”S ENGINE
IDI: Na gode nawaa, zamu hade
YAU MAI MAGANI:
ahaa
A siya magani, siya….maganin basir, maganin shawara, tablet din ido a siya.
MAMAN AMINA: Mai magani, yauwa zo, don Allah bani magunguna nan. Dama zan je wurin Dr Bala anjima na siya, amma tun da na ganka, shikenan kawai.
(WOMAN 1 HANDS HIM THE
PRESCRIPTION SLIP THE NURSE GAVE HER)
YAU MAI MAGANI: Haba, wane Dr Bala, someone that even comes to buy medicine from me, don’t worry, I am your one stop shop for every medicine you need.
(Even while unable to read the text). Wai, wai wai, gaskiya magunan na naki dukan su akwai su. Ama sai dai tsadan bala’e bale na uku’n nan,
MAMAN AMINA: Toh, fa, how much are the drugs?
YAU MAI MAGANI: Walahi dai, kin ga wannan, tutolin din nan, dari biyar ne, ga wata chloroquine nan, shi dubu biyu ne, sai kuma na kasan nan, butasolodene, shi ma dubu biyu ne, kin ga dubu hudu da dari biyar kenan.
MAMAN AMINA: Hanya kuwa mai magani, sune kuwa?
YAU MAI MAGANI: Kei, don Allah kar ki raina min wayo, ban gane ba, sune mana. Shekaru biyar kenan fa nna siyar da magunguna, baa abin da za ki gayamin da ban sani ba.
MAMAN AMINA:
SOUND: BABY CRYING Toh shikenan, yi hakuri, miko min su.
WOMAN 1: Yi hakuri Nna, ga magani na siya, zo muje kasuwa sai ki sha kin ji, yi hakuri.
Yauwa Mai Magani, Allah ya sa magungunan nan na ka, kwarai ne.
YAU MAI MAGANI: Haba Anty na, kar ki ji komai, wannan Maganin “conpam”ne!
SCENE TWO: ACT ONE. LOCATION.EXT (MORNING)
SOUND: THE CLATTER OF METAL PLATES AND OF MEN TALKING
AUDU: Yauwa Fatima, don allah ban tuwon nan
FATIMA: Tuwon nawo zaa baka?
AUDU: Kawo ta dari biyu da nama
FATIMA: Ruwan pampo ko pure water?
AUDU kei, wai yau ina maman ki ne? ai ta saba hadomin, kin cika mun kunuwa da tambaya. Hado min komai da komai na dari biyu kawai hahahah
FATIMA: Baba ne bai jin dadi, sai ya sa yau mama ba
ta shigo ba. Shikenan, gaa tuwon zaa kawo maka.
AUDU: Ayyah, Allah ya bashi lafiya.
SOUND: CRYING BABY.
(MAMAN AMINA WALKS INTO THE STALL WITH HER CRYING BABY)
FATIMA: Mamman Amina, haba don Allah, sai yanzu
zaki zo wurin aiki, haba ko kin gan sabi da mama ba ta nan ne.
MAMAN AMINA: Yi hakuri fati, walahi ba haka bane, Amina’n ne bata ji dadi ba, sai da na kai ta wurin nurse Ramatu a can health centre, dawo wan mu kenan. Hajiya yau ba ta shigo bane?
FATIMA:
Ayyah, walahi ban sani ba, sai ya sa na ji shiru. Eh walahi, Baba ne bai dan ji dadi ba, ta tsaya a gida yau
AUDU: (IN A LOUD ANGRY VOICE) Wai ina abincin ne.
FATIMA: yi hakuri, gashi nan zaa kawo maka,
Ungo, mamam Amina, don Allah gashi ki mika ma sa.
AUDU: Mutum da kudin sa, sai ma anmai yanga, toh walahi gobe ba zan dawo nan ba, haba ban san wulakanci.
MAMAN AMINA: Yi hakuri Mallam Audu, da ni take Magana, sai ya sa.
AUDU: Ba komai Maman Amina, yaa jikin Amina yanzu?
MAMAN AMINA: Da sauki
AUDU: Toh, Allah Ubangiji ya bata lafiya
FATIMA: Toh, wai mai nene asalin abin da kei damun Amina ne
MAMAN AMINA: walahi, ji na ke kamar hakori ne, jikin ta zafi, kuma tana zawo.
FATIMA: lalle kam, ba mamaki hakori ne, Amma wane irin magunguna a ka rubuta mata?
MAMAN AMINA: ga takardan nan, wanda Nurse Ramatu ta rubuta min, kuma gasu nan, na siyo daga wurin mai magani da kei tala.
FATIMA: Babban Magana, wace nurse ce ta rubuto maki wan nan magunan ma wa Amina? Kuma wani mai magani yace maki su ne wan nan?
MAMAN AMINA: Wallahi Nurse Ramatu ce, kuma gun Yau mai magani na siye su, yanzun nan kuwa.
FATIMA: Toh, bari ma na gaya maki gaskiyan Magana, in har kina san ran yarinyan nan, kar ki kuskura ki bata wadan nan magungunan nan, sabi da na daya.
Maganin da Nurse ta rubuta maki basu da hallaka da abin da kei damun Amina, na biyu magunan da Yau mai Kwaya ya siyar maki, ba ma abin da kei cikin takadar magani bane.
MAMAN AMINA: Inalillahi wa ina illaehi rajiun, wai wai, kuma fa sai da na tambaye ta, har ta fara mun fada, wai mei mei, tayi shekaru a cikin aikin nan, ta san mei ta ke yi, waya mutu, waye tashi..
FATIMA: saurara ki ji, toh wallahi bari na gaya maki abi na uku, duk magungunan nan da ki ka siya, duk sunyi expire!
SOUND: MAMAN AMINA WAILS AND CRIES TILL FADE
THE END
EPISODE FOUR
ACT ONE. SCENE ONE. LOCATION: EXTERIOR (EVENING)
SOUND: THE REV OF A TRICYCLE
FATIMA: Mallam Idi, tafiya ne?
IDI: Tafiya ne, ina zaa kai ki? Ko gida za kije ne
FATIMA: eh walahi, yanzu ma maman Amina ta tafe
gida, yau mun dan yi yanma gaskiya
IDI: toh. hau muje na ijiye ki
FATIMA: yauwa na gode Mallam Idi
(IDI IS UNABLE TO START THE TRICYCLE AS HE IS UNEASY AND DROWSY)
FATIMA: Wai, tsaya tukun Mallam Idi, yau lafiya
kuwa, naga kamar ba ka da nutsuwa yau sosai.
IDI: Yarinya kwanta da mind din kin, shekaru
biyar kenan, nna aikin nan, baa abin da zaki gaya min
Kin zauna sosai, toh ,muje
SOUND: THE CRASH OF A TRICYCLE, FATIMA WAILS
FATIMA: Wayo, kai na, kafa na! inalillah, haba Mallam Idi, mei haka, ko dei yau a maye kake ne
IDI: Don Allah kar ki reina min hankali mana, kawai dan wannan fadiwan shine zaki fara mun maganganu, dan Allah tafi nan. Kuma duk laifin ki ne, kei ce baki zauna sosai ba.
FATIMA: Da na karye fa, Allah ya dei sawake.
IDI: kei, an fasa tafiyan, ki je da kafa
FATIMA: Dama, ai bazan bika kuma ba, sabi da ban san
abin da ka sha yau ba gaskiya
SOUND: THE REV OF ANOTHER TRICYCLE’S ENGINE
AUDU: (TO FATIMA) Lafiya kuwa Fatima, yaa nagan ki duk kura haka, ko wani abu ya faru ne?
FATIMA: Mallam Audu, walahi Mallam Idi ne ya ka dani a babbur, daga ya kai ni gida, sai gururrum a kasa, adaidaita sahu ya kife kasa, walahi abin mamaki, kamar ba shi ba
AUDU la la la, ashe kei baki da labari Fatima, ai Idi yanzu ya fara shaye shaye, Ki gode wa Allah bai yar da kei a cikin gutter ba, kuma kafan ki bai karye ba.
FATIMA: haba don Allah, nima abin ya ban mamaki ba kadan ba, wai, yaushe Idi ya zama haka, gashi matan sa ta na da hankali sosai
AUDU: Toh, walahi, na kira sa, na mai Magana, duk iska ya bi, ko a jikin sa.
FATIMA: Ga shi na ga duk bakin sa ya fara lalace wa, ashe shaye shaye ne. Wai, Allah ya sawake.
AUDU: Yanzu hau dei muje na ajiye ki a gida.
FATIMA: kawai ka ajiye ni wurin Dr Bala,ya duba mini kafan nan, na dan buga shi a kasa, san da mu ka fadi yanzu, daga nan, kawai sai na karasa gida a kafa.
AUDU: Toh Bismillah.
SOUND: THE SOUND OF THE TRICYCLE’S ENGINE AS THEY RIDE OFF
ACT ONE. SCENE TWO. LOCATION: INTERIOR (EVENING)
DR BALA: (IN A LOVING VOICE) Fatima na wa, ai yau ban san zamu hadu ba, na sha sai gobe ne?
FATIMA: Walahi Idi ne ya kaa dani a kan babbur din sa, ashe ya je ya sha kwaya ne ban sani ba, duk jikan sa rawa yake
DR BALA: Auzubillah, Allah ya sa bai ji maki ciwo ba
FATIMA: ai sai ya sa nazo ai, ka dan duba min ciwon nan, ka sa min ko da GV ne da plaster.
DR BALA: Amma wannan Idi’n nan, bai da hankali, rabin raina ne zai karya wa kafa, Allah ya isa walahi
FATIMA: (GIGGLES), wai rabin ran sa, ai ni fa har yanzu ban yarda da kai ba. Irin ku haka, zaku rin ga wa mata karya.
DR BALA: haba Fatima, ni fa na sha an wuce zancen nan, walahi san ki na ke, kuma aure na ke so, tun yaushe nace maki, ki bani daman kawo gaisuwa gidan ku, kullun sai ki ce min, ba yanzu ba, kuma gashi lokaci na ta tafiya.
FATIMA: Toh Bala, na ji maganan ka, zan wa mama na Magana kuma, ka dei san shi Mai Anguwa, sai a hankali, bai ma san yaji maganan aure yanzu tin da ka ga ban gama karatu ba.
DR BALA: Shikenan, Allah ya kaimu, ni fa Fati, Wallahi in ba kei ba, sai rijiya kawai.
FATIMA: (GIGGLES ) Bala na wa kenan.
DR BALA: Ga shi, na maki dressing din ciwo din, ga kuma paracetamol ki sha in kika je gida.
Bari na zo na raka ki.
FATIMA: Kar ka damu, bari na je da gudu, na dan makara, mama za ta fara damuwa ban shigo da wuri ba, zamu hadu gobe ke nan, in shaa
Allah.
DR BALA: Allah ya tashe mu lafiya darling na.
ACT ONE. SCENE THREE. LOCATION: INT (EVENING)
SOUND: A DOOR OPENING AND CLOSING
FATIMA: Sannu da gida mama
HAJIYA MAIMUNA: Fatima, sannu da dawo wa, yaa kasuwa? Ko
FATIMA: Kasuwa lafiya mama, mun gode wa Allah.
HAJIYA MAIMUNA: Amma fa kin dan dade, lafiya dei ko?
FATIMA: Walahi mama, matsala a ka dan samu.
HAJIYA MAIMUNA: Matsala? Mei ya faru Fatima?
FATIMA: Walahi, na taso da ga shago kenan, sai na
hadu da Mallam Idi, ya ce zai kawo ni gida.
HAJIYA MAIMUNA: Wane Idi kenan?
FATIMA: Idi dei, Mai Adaidaita sahu, mijin mai Mana wanke wanke.
HAJIYA MAIMUNA: Toh, Toh, shi fa, na gane shi, toh sai a ka yi yaya?
FATIMA: walahi nna zama kenan, sai gamu a kasa, har na dan ji ciwo a kafa
Yayi fushi ya tafi, wai duk laifi na ne, baga sai Mallam audu ya zo wuce wa ba, ya gan ni duk kura, ai shine yazo ya ke gayamin ce wa ai Idi ya fara shayeshaye.
HAJIYA MAIMUNA: Auzubillah, Baki dai ji ciwo ba dei ko?
FATIMA: Na dan buge kafa, amma Mallam Audu ya
kaini gun Dr Bala, ya dan gyara min ciwo kuma ya bani magani. Ba komai mama
HAJIYA MAIMUNA: Toh Mun gode wa Allah, Allah yaa ci gaba
da kare mu. Saanu Fatima, Allah ya maki albarka
FATIMA: Amin Mama, Ya jikin baba, ya dan ji sauki kuwa?
HAJIYA MAIMUNA: Toh, Ba laifi, ya dan samu yayi bacci, yanzu ma bai tashi ba, daga dakin sa nake.
FATIMA: Toh, Allah ya bashi lafiya, amma fa ya
kamata a kai shi asibiti cikin gari a duba mei ka damunshi.
HAJIYA MAIMUNA: Ba wani abu bane, kawai ciwon hakori ne, kuma ya ragu, amma gobe zamu je health center da shi, mu je mu ga Dr Bala ko Nurse Ramatu.
FATIMA: Yauwa, ya fi. Allah ya kai mu gobe, Amma fa Mama ban yarda da Nurse Ramatu ba fa, sai dei dr Bala, sabi da yau maman Amina ta je can wurin su a ka hado mata wasu irin magunguna wai maganin hakori wa yarinyan ta, kuma walahi mama duk magunan basu da alaka da abunda ke damun yarinyan
HAJIYA MAIMUNA: Toh, auzubillahi, shikenan, sai mu jei wurin Dr Bala din gobe kenan.
FATIMA: Balle, Mama, akwai wata magana fa.
HAJIYA MAIMUNA: Maganan mei kenan? Lafiya?
FATIMA: Lafiya kalau, Mama maganan aure ne, kin fa tuna na gaya maki Dr Bala ya ce ya na sona da aure, kuma har yanzu baki yi ma baba Magana ba.
HAJIYA MAIMUNA: Wai, har gaba na ya fadi, Fatima, kin san
Baban ki ba zai bari ki yi aure ba sai fa kin
gama jamiia, duka duka ba shekara daya rage ba, ki yi hakuri, in kika gama, sai a fara zancen aure. Ko ba haka bane?
FATIMA: (SOBBING) Ni Mama, gaskiya ba zan jira ba, a min aure kawai, in ya je ya samo wata fa, ai ni nayi asara kenan
HAJIYA MAIMUNA: ba wani maganan asara a nan, in dei Allah ya ce shine mijin ki, Ba abin da zai hana.
SOUND: FATIMA GRUMBLES AND LEAVES THE ROOM ANGRILY.
HAJIYA MAIMUNA: hmmmm, Fatima kenan, yarinya bata gane bane, matar mutum kabarin sa, kuma ba wanda zai aure matan wani sai dai na shi. Hakuri Fatimatu, hakuri.
EPISODE FIVE
ACT ONE. SCENE ONE. LOCATION: INTERIOR (MORNING)
SOUND: PATIENTS CHATTING IN FRONT OF THE HEALTH CENTRE AS DR BALA WALKS IN
DR BALA: Good morning everyone, an tashi lafiya?
Please can the women sit on the chairs in front while the men take the chairs at the back, when I call next, I want a male first, and then a female.
I hope we all understand?
PATIENTS: (CHORUS) Eh Mun gane
DR BALA: Toh, na miji daya, bisimillah
SOUND: MAMAN AMINA STORMS THE CENTER SHOUTING EXPLETIVES AT THE DR
MAMAN AMINA: you bloody murderous people, where is that witch that calls herself a nurse and a Dr all in one, wicked woman, where are you? Come out now and let me expose your secrets to the world.
DR BALA: Calm down, woman, come inside please and tell me what the problem is.
MAMAN AMINA: Noooo, come inside? Which inside? The same inside that I came and they wrote nonsense as medication for my child? That witch of a nurse better come outside now else I will burn this place down.
PATIENT 1: Madam calm down na, listen to the Dr please.
PATIENNT 2: Ah, Madam please don’t burn this place down o, this is the only primary health centre serving two villages, if you burn it down, where will we go to for medications.
PATIENT 3: Balle, where do you even intend to see fuel to burn this big building down, madam please
whatever the problem is, go inside and talk to the Dr
MAMAN AMINA: Please, excuse me, all of you saying I should calm down, do you know that this people nearly made me lose my child. Do you know?
Infact, I don’t have any case with you, I am marching straight to the mai anguwa’s house.
DR BALA: Ah. Madam, please, don Allah, shigo ciki muyi Magana, come inside lets settle this amicably.
MAMAN AMINA: inside abi? Oya bisimillah, let’s go inside.
SOUND: DOOR OPENS AND CLOSES
DR BALA: Madam, please calm down and explain to me
what actually happened.
MAMAN AMINA: Yesterday, I came here with this child, look at this child; she is barely a year old, she had teething problems and a fever, but look at the prescriptions she wrote me, take a look at this. What sort of nonsense prescription is this?
DR BALA: I am sorry woman, I am sure the Nurse must have made a mistake, I sincerely apologize on her behalf, now please hold on let me take a look at your child and prescribe some other medicine, please.
MAMAN AMINA: here, ga ita nan
DR BALA: It’s okay madam, yes, the baby has a small fever and well, yeah some teething problems, because they are just sprouting, nothing to do about that, but you can just buy some paracetamol syrup from the guy that sells drugs down the street.
MAMAN AMINA: which guy? Do you mean Yau Mai magani?
The same idiot that sold me these drugs as what was written on the prescription? There is no way I am going back to that retard, and even if I am, it will be to inform him that the mai Anguwa wants his head for supper.
DR BALA: Haba, dei, don’t worry woman, I will look into the matter, there is no need to report to the Mai Anguwa nor go back to see Yau mai magani. I will have a word with him. Meanwhile how much did you pay for the medicine, tell me please so I can refund you.
MAMAN AMINA: Four thousand five hundred naira.
SOUND: DR BALA COUNTS SOME MONEY AND HANDS TO HER
DR BALA: Here is the money, please ensure that
whatever happens here remains here let this not go beyond these walls, don Allah.
Meanwhile, I think I have some paracetamol
syrup for your child in my bag. Let me check
SOUND: RUMMAGES THROUGH HIS BAG FOR THE SYRUP
DR BALA: Yauwa, gashi nan, don Allah a yi hakuri
MAMAN AMINA: Ba komai likita, ya wuce. Na gode sosai.
SOUND: DOOR OPENS AND CLOSES AS MAMAN AMINA EXITS
DR BALA: kai kai, waayo, so this woman wants to ruin this business for us, haba, who prescribes such medicine for an infant? auzubillah, and that useless Yau, I am sure he must have been high on some stimulants. They will both be hearing from me.
Neeeeeext!
PATIENT 1: Good morning Dr
DR BALA: Good morning, what can I do for you?
PATIENT 1: Doctor, actually Dr, my gum has been bleeding, each time I spit, it comes accompanied by some blood, its becoming embarrassing and its even worse when I brush in the morning.
DR BALA: ah, I know what you have, its called “dental conjunctivitis sclerosis”, and gaskiya the cure is very expensive, that is if we do not extract the tooth ba.
Now come close, let me take a look
PATIENT 1: Ah, extract ke? Please help me Dr, I don’t want my tooth extracted, please help me.
DR BALA: I think you have been eating too much rubbish food, haba Mallam, you aren’t supposed to eat more than twice a day, and you should eat a lot of yams and palm oil, and ensure that you use some methylated spirit to rinse your mouth once in a while.
PATIENT 1: Haba Dr. too much food kuma? Well, what do we do now? How can we stop the bleeding?
See, its bleeding already again, kai this is not good walahi
DR BALA: So, now you will have to pay consultation fee, so I can write the prescription for you, luckily for you, we don’t have to extract the teeth just yet, but maybe lat koer, we still need to
PATIENT 1: Ah. Alhamdulillah, how much is the consultation fee?
DR BALA: It’s one thousand naira only
PATIENT 1: Okay Dr, thank you. Here is it.
DR BALA: So, you will go buy these drugs, but if you want to pay for them now, you can come pick them up at my chemist later.
PATIENT 1: Let me just pay for them now, how much will the medicines cost me?
DR BALA: Just two thousand naira only.
PATIENT 1: okay, here, have the money. I will come by in the evening to pick up the medicine. Thank you Dr
DR BALA: You are welcome.
Neeeext!
HAJIYA SARATU: Good morning doctor.
DR BALA: Good Morning madam, how are you this morning?
HAJIYA SARATU: fine doctor, but not very fine, I was here a few days ago and met Nurse Ramatu who was really rude to me, she didn’t even let me tell her what my problem was before she rudely dismissed me. That woman acts like a witch, her cup is almost full in this town, I will make sure I bring her reign to an end, she doesn’t know me, I have heard so much about her and I am very ready for her.
DR BALA: Oh wow, I am really very sorry about that, I am sure she was probably in a bad mood, she isn’t always like that.
So what could be the problem?
HAJIYA SARATU: Dr walahi I can’t chew anything with this left part of my mouth, I know there are holes in it because sometimes I get to pick out food items from them and it’s so painful
DR BALA: Okay I see, come closer let me take a look at your teeth
Ah, open your mouth, ah, okay I see, well, you have what is known as “Rental scabies” and as it is now, we may need to take out these teeth as quick as possible before they affect the rest.
HAJIYA SARATU: Wait, I don’t understand, you want to extract my teeth because it has holes in them, but that wasn’t what the last dentist I saw in the city told me, I was told I could get it filled by any dentist anywhere whenever I was ready, so I don’t quite get why you are not giving me the filling option.
DR BALA: ah, well, madam I am sorry, the holes in your teeth are so big that no amount of sand and cement can fill it, I am afraid that’s all that can be done now
HAJIYA SARATU: So, let’s say I want the teeth removed, can it be done now?
DR BALA: yes yes yes, why not, I have all my tools here, would you like for the teeth to be extracted now? Or you want to come by my “hospital” later?
HAJIYA SARATU: Hospital? Oh really, you have a hospital?
Where is that?
DR BALA: yes I do, it’s at the end of the street where the market is, you can’t miss it. It has a big sign with DR BALA CLINIC written on it.
HAJIYA SARATU: okay, that’s fine. I will drop by in a few days to get the teeth extracted.
DR BALA: I will be expecting you madam.
SOUND: DOOR OPENS AND CLOSES AS HAJIYA SARATU EXITS
DR BALA: (MONOLOGUE) I better be careful with this woman, she looks like she is out to ruin business for us, who is she sef? Haven’t seen
her around before, but she seems to know us very well, I will make my findings and make sure she doesn’t see to it that we become expired!
Neeeeeext!!!
THE END
Translation - Hausa MAGANIN RASHIN SANI....
Fassara: Mohammad Aliyu Umar
Yan Wasa:
DR SEYI: Matashin likitan hakori ne da aka tura shi asibitin sha ka tafi na unguwar dawaki don bautar kasa, bai jima da kammala aikin gwajin likitanci ba a asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano.
MAI-UNGUWA: Dattijo ne dan shekara fiye da hamsin, shine mai unguwar Dawaki, kuma bashi da ilimin boko.
HAJIYA MAIMUNA: Matar Mai unguwa ce, kuma tana saida abinci a tashar motar Unguwar Dawaki.
NURSE RAMATU: Ta koyo aikin jinyar ta ne a kanan asibitocin birni, inda kuma take taimakawa marasa lafiya a asibitin Sha ka tafi na kauyen su tunda babu kwararrun likitoci, sai yan bautar kasa da ake turawa lokaci zuwa lokaci.
DR BALA: Yaron likitocin hakori ne wanda ke taimakawa manyan likitocin hakorin aiki a asibitin Sha ka tafi, Amma yakan nuna yasan komai. Yana hada Kai da Ramatu ma'aikaciyar jinya suna damfarar mutane, duk lokacin da baya asibiti to yana shagonsa da yake Kira CHEMIST yana cirewa mutane hakora, koda yake bai taba zuwa makaranta ba, kuma da yanda yake kwaba turancin sa na bawa mutane dariya, Amma kullum cewa yake a Amurka yayi wo karatunsa.
FATIMA: Ya daya tilo ga Mai unguwa, kuma tana karatu a jami'a a cikin birni, sai dai tana yawan zuwa gida don taimakawa babarta harkokin yau da kullum, kuma suna Soyayya da Dr Bala.
YA'U MAI MAGANI: "Kafada Dr" kenan kamar yadda yake Kiran kansa, kayan maganin maye yake saidawa yan shaye shayen garin, Wanda yake sarowa a gun Dr Bala kuma duk magungunan sai sun lalace yake sayar masa, Amma yakan fake da cewar magani sahihi yake sai dawa mutane.
IDI: Dan adaidaita sahu ne, kuma babban kwastoman Dr Ya'u ne, kullum yana cikin maye.
AUDU: Shima dan adaidaita sahu ne, mutumin kirki ne, harkar neman abinchi tasa ya zama abokin Idi.
MATA 1: Kanwar Mai Unguwa ce, kuma tsayayyar mace da bata daukar wasa, tana aure a makotan Unguwar Dawaki Amma tana kawo ziyara akai akai gida.
MATA 2: Matar Idi ce kuma, kuma tana yiwa Matar Mai Unguwa aikatau a Tasha wajen sayar da abincin ta.
KASHI NA FARKO....
FITOWA TA FARKO: A WAJE DA SASSAFE:
(A GABAN ASIBITIN SHA KA TAFI, LAYI BIYU AKA KAFA A BAKIN ASIBITIN DAYA NA MAZA DAYA NA MATA, DUK SUNA JIRAN RAMATU MALAMAR JINYA, DON TA SAURARE SU TAJI ABINDA KE DAMUN SU KUMA TA DORA BISA MAGANI, HAKAN NA FARUWA DUK, RANAKUN LITININ, LARABA, DA KUMA JUMA'A).
SAUTI: Daga can nesa ana jiyo tarin daya daga cikin marasa lafiya dake Kan layi.
MUTUM 1: ( YANA MAGANA DA MUTUM NA 2) Wai Anya kuwa Matar nan zata zo yau? Haba Dan Allah, wasun mu fa tun 6:30 na safe muke nan.
Har yanzu bata zo ba, sai anyi magana kaji suna cewa gwamnati bata aiki, kuma fa Wai Nan gaba zata zo, ka duba ka gani yanzu fa 9:00 na safe.
MUTUM 2: Wallahi kuwa, aini badan birni ya min nisa ba da asibitin Murtala zan tafi, kuma kaga sun ma daina turo masu bautar kasa, rabon da su turo wani yau shekara biyu fa da suka gabata.
Wai Malam Kai meke damunka ne ma?
MUTUM 1: Wallahi malam dasashi nane ke kumbura yan kwanakin nan, kuma na sayi asuwaki Ina amfani dashi ko na samu sauki Amma abin yaci tura shine na zo naga Likita Ramatu ko ta bani maganin sa.
MUTUM 2: Wai, ikon Allah nima fa haka nafuskanci wannan matsalar watan da ya gabata, Amma da naje wajen Dr Bala ya min wani hadin tuni na samu sauki, sai dai fa da abun ya dawo ciwon kamar zanyi hauka, Allah ne Ya taimake ni wallahi na zata sai na ciren hakori.
SAUTI: MASHIN DIN ADAIDAITA SAHU NA KARASOWA WAJEN:
(Karfe 9:00 Ramatu ta shigo asibitin rike da jaka)
NURSE RAMATU: Ina kwanan ku, kun tashi lafiya? Kuyi hakuri nayi latti kanina na Kai asibiti cikin gari, anma kwantar da shi.
MATA 1: Ayyah Allah Ya ba shi lafiya, sannu da zuwa likita.
MATA 2: (CIKIN ALAMAR TAMBAYA) Amma likita wace irin cuta ce haka ke damun sa da har sai kin kaishi birni? Bayan kunce ke da Dr Bala babu ciwon da zai gagare ku, ko dai abin naku bula ce, kuma fafa ce?
SAUTI: RAMATU TAYI TSAKI AKA JIYO KARAR BUDE KOF DA MUKULLI, BUDE KOFA DA RUFEWA)
FITOWA TA BIYU: (CIKIN ASIBITIN, DA SAFE)
(RAMATU TA ZAUNA A GABAN MUTUM 1, A CIKIN OFISHIN LIKITA)
NURSE RAMATU: Malam me ke damun ka?
MUTUM 1: Ranki shi dade, satin nan da ya gabata na wanke baki na da gawayi, sai naji yana min zafi, hakan ya sa na sayo asuwaki a kasuwa na fara amfani da shi, Amma ga mamaki na sai dasashi na ya fara kumbura kuma yana fidda jini,hasali yanzu ma jini bakina yake.
NURSE RAMATU: To, bude bakin ka. (TA YAMUTSE FUSKA CIKIN DAMUWA) Malam wannan hakorin naka ai ya rube wallahi! Gaskiya kaje gun Dr Bala ya cire maka shi.
Neeeeeeeeeext!
MUTUM 1: Likita tsaya mana, ban gane ba, Kina nufin naje na cire hakorina? Tab! Babbar magana, wai ba wani MAGANI da zaki bani na samu saukin ciwon nan ne Dan Allah?
NURSE RAMATU: Wallahi a'a, kawai kaje gun Dr Bala ya cire maka Malam, kwararran likitan hakori ne, kuma dubu daya fa zaka bada amaka tiyatar nan, Dan Allah matsa ka bawa wasu waje su shigo.
(SAUTI: CIKIN FUSHI MUTUM 1, YA TURA KUJERA TAYI KARA, SANNAN YA FICE CIKIN FUSHI YA BUGO KOFAR OFISHIN, CAN BAYAN WANI LOKACI MATA 2, TA SHIGO).
NURSE RAMATU: Sannu da zuwa, meke da mun ki?
(TA KALLI MATAR TAKE TA GANE ASHE WANNAN MATAR CE DA TAKE GULMAR TA DAZU, DON TACE TA KAI KANIN TA ASIBITIN CIKIN GARI).
Neeeeeeeeeext!
MATA 2: Ahn ahn likita, amma ni ai baki duba ni ba, kuma naga kina Kiran wa ni, haba Dan Allah.....
(SAUTI: KARAR MOTSIN KUJERA).
Likita ki taimaka min wallahi bani da lafiya....
NURSE RAMATU: To me kike so nayi akai!? (TA SA HANNU TA KARO SAUTIN RADIO DAKE BISA TEBURIN TA DON MA KAR TAJI KORAFIN DA MATAR TAKE MATA).
Kin ga malama, bani da lokacin da zan saurari surutanki, babu abinda ya dameni, koma mai yake damunki ya kashe ki mana.
MATA 2: Ah! Nas, shin nayi miki wani laifi ne? Wane irin laifi zan iya aikata miki kuwa? Ikon Allah.
NURSE RAMATU: Au au au au, Watau wane irin laifi zaki iya aikata min ko? (TA SA HANNU TA RAGE SAUTIN RADION) Watau ke kin zo bayan kin gama yi mini dariya da wulakantani don na kai dan uwana asibin cikin birni ko? Tunda ni ba zan iya biya miki bukatunki anan ba, toh mai ya zaunar dake anan kema zaki iya tafiyarki cikin garin ai. Shikenan
Wata ta shigo!!!!!!!!!
MATA 2: (TA FARA HAYANIYA TANA ZAGE ZAGE TANA SON RIGIMA DA NURSE RAMATU) Allah ya isa, maiya. Sai na tona asirinki a cikin garin nan kowa ya san cewa ke macuciya ce, Nas din karya ce. Uhuhuhuhuhuhuhuhuhuhuhu, idan har kin san zaki iya me ya sa ki ka dauki dan uwanki ki ka kai cikin birni?
Sai Mai Unguwa yaji labarin nan. Duk na san sirrrinki. Bari na je na dawo garin nan, zan samu lokacinki. Maiya kawai.
NURSE RAMATU: Wani ya shigo!!!!!!!!!!!
(NURSE RAMATU TA HAMKADA MATAR WAJE SAN NAN TA RUFO KOFA DA KAR FI, SAUTIN RUFE KOFA YA FITO SOSAI)
(KOFA TA SAKE BUDEWA MUTUM 2, YA SHIGO)
MUTUM 2: Ramatu Nas ina kwana?
NURSE RAMATU: Ina kwana, toh, kai ne? Me kuma ya faru da kai a wannan karon?
MUTUM 2: Kwanakin baya ne na dan yanke a kafata, sai na zuba kalanzir kadan don jinin ya tsaya daga baya kuma na shafa ruwan ganyen bishiyar dogon yaro da kashin shanu kadan, amma bayan dan wani lokaci sai ya ciwon ya fara yin ruwa mai tsananin wari. Kuma radadin ciwon ya dada karu wa shima.
NURSE RAMATU: Kai kai kai kai, innalillahi wa inna ilaihi raji’un. Ai Malam, billahi lazi kafar nan ta gama rubewa, sai dai a yanke ta a sa maka ta roba.
Fita ka baiwa sauran mutane wuri. Don Allah ka fita waje ka baiwa mutane wuri su shigo ciki.
Wata ta shigo!!!!!
MUTUM 2: Innalillahi wa inna ilaihi raji’un, innalillahi wa inna ilaihi raji’un, Nas, yanzu shikenan sai an yanke mun kafata kenan?
Don Allah Nas, don Allah ki taimaka min, karki ce babu abinda za a iya, don Allah.
SOUND: MTUMIN YA KAMA KUKA, A HAKA YA FITA YANA KUKAN
NURSE RAMATU: (CIKIN YAMUTSA FUSKA DA GYATSINE) Mmmscheewww, sha sha sha, idan aka ce muku ku zo asibiti a yi muku maganin da ya dace ba zaku zo ba, yanzu gashi kafarsa ta rube kuma babu abinda zan iya yi mishi akai.
Wai, waye yakamata ya shigo ne wai?
Wata ta shigo!!!!!!
SOUND: JARIRIYA NA KUKA LOKACIN DA WATA MATA KE SHIGOWA OFISHIN.
MATA 1: Nas Ramatu, Ina kwana.
NURSE RAMATU: An tashi lafiya? Me yake damun jaririyar ta ki ne?
MATA 1: Nima dai ban sani ba, na dai lura da cewa kamar hakori take son ta fara yi; sun riga sun fara tsirowa, ta kwana biyu tana dan yin zazzabi yanzu.
NURSE RAMATU: Ayyah, sannu ‘yar yarinya.
MATA 1: Ba ta bacci da daddare, sai dai tayi ta mutsu-mutsu kuma jikinta sai ya dinga yin zafi sosai lokaci zuwa lokaci. Ki taimaka mana don Allah.
NURSE RAMATU: Kash! kuma gashi bani da allurar fitar hakori anan da na bata. Amma kin ga abinda yakamta kiyi ko, zan rubuta miki magunguna, akan hanyarki ta zuwa kasuwa akwai wani shagon sayar da magani can kasan hanyar, kullum yana nan, ki gaya mishi ya baki farasitamol da folik asid da ibuprofen, idan kuma baida su sai ki saya a gurin matashin nan mai yawon tallan magunguna a kasuwar. Ke ko a ina ma kike so, ke dai ki siya ki bata da wur-wuri. Ki baiwa ‘yar taki ba zata dauki lokaci ba zata warke.
Wani ya shigo!!!!!!!???
MATA 1: Ah, Nas amma ai duk wadannan kwayoyi ne fa, yarinyar nan ko shekara daya ba ta kai ba, na dauka magani na ruwa zaki ba ta, har allura fa kika ambata duk a ciwon hakorin?
NURSE RAMATU: Ke matar nan, bani da lokacin wannan shiriritar, idan ba za kije ki sayi wadannan magungunan ba duk abinda ya faru da ‘yarki babu ruwana.
Wai tsaya, shin kin dauka ban san abinda nake yi bane? Shekaru goma nayi ina koyon aikin nan, sai ki gaya min shekaru nawa Babban likitan lafiya yakeyi a makarantar nazarin kula da lafiya? Bari na gaya miki ni na wuce cancanta ma. Kin ga fice mini daga ofis, na gama da ke da ‘yarki!
SOUND: AKA SAUKI SAUTI
KARSHE..............
KASHI NA BIYU
FITOWA TA FARKO: DR BALA ZAUNE CIKIN DAKIN SHAN MAGANINSA, CIKI, SAFE.
(DR BALA ZAUNE CIKIN DAKIN SHAN MAGANIN SA INDA YAKE CIREWA MUTANE HAKORI, YAKE BASU MAGANI, HARMA YAKAN CE YANA DA MAGANIN KOWACCE IRIYAR CUTA CE)
MUTUM 1: Dafta Bala ina kwana?
DR BALA: Ina kwana Malam, yaya iyali? Me zan yi maka da sassafen nan?
MAN 1: Wallahi Likita, na je karamin asibiti ne ban same ka a can ba, kuma ka san tun lokacin da gwamnati ta daina kawo ‘yan bautar kasa karamin asibitin nan, muke cin albarkacinku kai da Ramatu Nas.
DR BALA: Gaskiya wannan jawabi naka gaskiya ne kuma abun dubawa ne ta kowanne sashe. Kana ji ko, a matsayina na mai kishin al’ummar garin nan, yana da muhimmanci mu bayar da tamu gudummawar wajen kulawa da lafiyar jama’a. Shi yasa mu ke garin nan, abinda gwamnati ba ta sani ba shine, ba zai yiwu a kwatanta mutumin da yayi karatu a kasar Amurka da wanda yayi karatu a Kano ba, Haba Malam, akwai banbanci fa!
MUTUM 1: Haka ne Likita, toh Likita wallahi ni dai wannan hakorin yana bani matsala sosai, bayan nayi amfani da asuwakin da na saya a kasuwa waccan karon sai matsalar ta karu. Shine naje gurin Ramatu Nas a karamin asibiti, shine tace babu abinda za a iya yi illa a cire hakorin da baida kyau.
DR BALA: Matso kusa bari na duba na gani.
SOUND: SAUTIN KARAR JAN TAKALMI YAYIN DA MUTUMIN KE MATSAWA KUSA DA DR BALA.
DR BALA: La la la la, wai. Malam tsaya daga nan, wai wannan warin, daga bakin ka ne haka. Magana ta lalace wallahi. Ai dole a cire hakorin da baida kyau dinnan cikin gaggawa kuwa.
MUTUM 1: Kai, innalillahi, yanzu Likita babu wani abu da zaka iya yin dole sai dai a cire hakorin nan?
DR BALA: Malam, bilahillazi ko an kai ka Amerika, dole sai hakoran nan sun fita.
MUTUM 1: Innalillahi wa inna ilaihi raji’un, toh yanzu Dr Bala, nawa zan kashe wajen cire hakorin nan?
DR BALA: Dubu daya ne cire hakori guda daya, kuma naga guda uku ne basu da kyau, ka ga ya kama dubu uku kenan, ga dubu daya kudin ganin likita, ga dari biyar kudin fom, ga wata dubu uku kudin maganin da zan baka. Kaga duka gaba daya ya kama dubu bakwai da dari biyar kacal.
MUTUM 1: Subhanallahi, haba Dr, kudin nan sun yi yawa fa, yanzu a ina zan samu irin wadannan kudade ina cikin wannan yanayin?
DR BALA: Toh ai shikenan, sai ka tafi ka ban wuri, yanzu ba uku bane su ka lalace, bayan sati biyu, duk bakin ka zai gama rube wa, zaka gane. Dariya a waje ma sai tayi maka wahala.
MUTUM 1: Toh shikenan likita, zan biya, a zo a cire. Ga dubu bakwai, su kenan, don Allah a yi hakuri haka.
DR BALA: (CIKIN JIN DADIN GANIN KUDIN) Shikenan, kwanta, ga benci nan bayan ka.
MUTUM 1: (YAYI ADDU'A CIKIN KASA KASA DA MURYA) Ya Allah ga bawan ka a hannun ka, ka taimake ni.
DR BALA: Malam, yau ni ne mai taimaka maka.
SOUND: (SAUTIN KARAR KARAFUNA, GUDUMA, DAN BUDA, DA ARAFTAKI SUKAYI KARA)
MUTUM 1: Tsaya, tsaya, tsaya likita, wai wa kake nufin ka daure da wannan katotuwar igiyar ne? Haba, ni fa ba Saniya bace.
DR BALA: Wallahi, ai kuwa kai din ne, ka natsu kawai mugama abin nan sharp sharp.
MUTUM 1: Wai Likita, tsaya ,tukunna mana,Ban game sharp sharp na, na ganka rike da guduma da araftaki da Dan buda, wai dutse kake niyyar farfasawa ne?
SOUND: AKA RINGA JIYO IHUN MASIFAR DR BALA DA BURARIN MAJINYACI, LOKACIN DA DR BALA KE KOKAWAR DAURE MUTUMIN HAR AKA SHUDE GURIN.
FITOWA TA BIYU: WAJEN DAKIN SHAN MAGANIN DR BALA, WAJE, RANA.
SOUND: SAUTIN MUTANE NA TASHI YAYIN DA SUKE TA ZIRGA ZIRGA A GABAN SHAGON DR BALA.(MUTUM 2 YAYI SALLAMA A SHAGON DR BALA).
MUTUM 2: Ina wuni Dafta Bala, yaya iyali, yaya aiki kuma?
DR BALA: Lafiya kalau Malam, yaya yau? Barka da shigo wa, kai kai kai, me ya sami kafarka haka? na ga har tsutsa ce ke fitowa daga ciki, innalillahi. Kai amma kafar nan ta rube.
MUTUM 2: (CIKIN BACIN RAI DA DAMUWA) Wallahi likita, daga wurin Ramatu Nas na ke, ta ce na zo na same ka, wai babu abin yi, sai dai a yanke ta kawai. Innalillahi wa inna ilaihi raji’un.
DR BALA: Mu yi sauri mu shiga ciki a yanke kafar nan da sauri kafin ta illata dayar, kasan irin wannan abun yana da saurin yaduwa sosai.
SOUND: SAUTIN BUDEWAR KOFA YAYIN DA DR BALA DA MUTUMIN KE KOKARIN SHIGA DAKIN MAGANI.
MUTUM 2: Innalillahi wa inna ilaihi raji’un, toh yanzu likita nawa ne kudin yanke kafar ne?
DR BALA: Dubu ashirin ne kawai, ga kuma kudin magani dubu biyar, kudin ganin likita dubu daya, kudin fom dari biyar kaga dubu ashirin da shida da dari biyar ke nan.
MUTUM 2: Innalillahi, Ya Allah ka taimake ni, ga kudin likita.
DR BALA: (YANA KIRGA KUDIN CIKIN FARIN CIKI), daya, biyu, uku…
Ashirin da hudu, ashirin da biyar, ashirin da shida.. Yawwa, sun cika, daidai. Toh, ga benci nan bayan ka, kwanta.
SOUND: SAUTIN HAYANIYA DA BURARI YA BARKE TSAKANIN DR BALA DA MUTUMIN DA ZA'A YANKEWA KAFA.
MUTUM 2: Waaayyyo Allah, waaayyyoooo, na mutu, waaayyyoo!!!!!
DR BALA: Ka tsaya tsam guri guda, nan da minti biyar mun kammala ai.
MUTUM 2: Tsaya, ni fa ban gane ba, kana nufin zaka yanke min kafa ba tare da ka fara bani maganin da zai dauke min radadin ciwo ba? Kai wane irin likita ne? Don Allah bani kudina. Bana sha’awar aikin kuma, na fasa. Haba!
DR BALA: Ba wani zafi da zai yi maka, zaka ji kamar mintsini ne kawai da zarar zarton ya ratsa ta cikin kasusuwanka, yanzu-yanzu zamu gama.
MUTUM 2: Tab! A’a nagode. Ina ganin gwara ka ci gaba da cire hakora amma banda yanke gabobin jiki, ni bani kudina kawai.
DR BALA: Ka san Hamisu Gurgu ko? Ni na yanke mishi kafa lokacin da ya kamu da cutar jeji a kafar.
Hatta Maman Sale ta daya garin can, ni na yanke mata mamanta guda daya itama. Na yi shekaru ina wannan aikin. Karka damu.
MUTUM 2: Eh duk na san su, kuma na san dukkansu mutuwa sukayi bayan ‘yan makonni da ka yanke musu gabobin jikinsu. Hmmn, watau duk jita-jitan da ake yi akanka gaskiya ne. Zaka girbe abinda kake shukawa nan bada dadewa ba, likitan karya macucin mutun kawai, bani kudina ko na dirka maka gudumar Nan.
DR BALA: Don Allah, don Allah, karka nemi ka ci mini mutuncim mana, ni ne shugaban likitoci kuma kwararre, a kasar Amurka na samo horo na kuma nayi aikyuka a asibitocin koyarwa daban-daban, karka zo ka nemi ka koya mini aikina, ba zan aminta ba. kwashi kudinka da rubabbiyar kafarka ka fice min daga asibiti.
MUTUM 2: Nan dinne kake kira asibiti? Mscchew
SOUND: MUTUMIN YA WARCI KUDIN SA YA BUGO KOFA YAYIN DA YAKE FICEWA DAGA KYAMIS DIN.
DR BALA: (CIKIN TAKAICI) Mutumin banza, yana neman ya ba ta min rai bayan yau da farin ciki na fara, Allah ya isa, kai, ji yadda tsabar kudi nera 26,500 ta kubuce min.
Kai, kai, kai. Amma gayen nan, dan iska ne!
SOUND: SAUTI KIDA DA WAKA HAR AKA SHUDE WAJEN....
FITOWA TA BIYU: CIKIN DAKIN SHAN MAGANIN DR BALA, CIKI, YAMMACI.
(NURSE RAMATU DA DR BALA ZAUNE CIKIN DAKIN SHAN MAGANIN SA, SUNA TATTAUNA ABINDA YA SHAFI HARKOKIN SU)
NURSE RAMATU: Yauwa wannan mai fama da warin bakin da rubabbun hakoran ya zo an cire mishi hakoran ko? Ai ni ce na turo shi, na gaya mishi kai kadai zaka iya taimakonsa.
DR BALA (YA KYAKYACE DA DARIYA) Wallahi kuwa, hakoransa uku aka cire, sun riga sun gama lalace wa, sai faman ihu yake yi kamar wani karamin yaro.
NURSE RAMATU: Kace yau kayi kasuwa kenan?
DR BALA: Gaskiya ba laifi, mun gode wa Allah, yaya asibitin? Inshaa Allahu gobe zan shigo.
NURSE RAMATU : Bala, don Allah ka san abin da ya kawo ni, sallame ni na kama gabana kawai.
DR BALA: Ehhehehe, Nas kenan, ai daman na sani, toh kin dai ga yau sai a hankali, hakori kawai na cire, kuma dubu uku na karba. Toh gashi, ga dubu daya. Na gode.
NURSE RAMATU: Kai Malam, kar mana ka raina min hankali, yaushe ka fara karya?
DR BALA: Haba Nas, Karya kuma? Wallahi shikenan abin da na yi tun safe.
NURSE RAMATU: Toh mutumin da za a yanke wa kafa da na aiko kuma fa? Don Allah bana san rainin hankali.
DR BALA: Tab! Wannan mutumin, ai wannan karshen bacin rai kenan, ko kinsan har sai da ya biya kudinsa, amma da ya hangi kaifin bakin zartona sai ya tsorata ya kama cewa sai na bashi maganin da zai dauke mishi zafin radadin da zai ji tukunna. Ba mamaki ya riga ya samu labarina ne shi yasa ya yanke shawarar fasa yin tiyatar. Na mayar mishi da kudinsa, kin san irin wadannan mutanen kiji tsoronsu zasu iya raba ki da sana’arki.
NURSE RAMATU: Haba? Toh, yi sauri ka bani nawa kason, cikin gari zan tafi, dan uwana Mukhtar ne baida lafiya yana kwance a can asibitin cikin birni. Ina son naje na zauna agurin shi.
DR BALA: Haba, mai ya same shi?
NURSE RAMATU: Zazzabi ne da ciwon kafa, haka kawai ya kasa tafiya.
BALA: Lallai, Ramatu Nas, wannan kawai yana nufin kafarsa ta lalace kenan fa! Gaskiya yana bukatar yazo a yanke mishi kafar nan tun kafin abun ya yadu ya kama hannuwansa. Don Allah ki je ki kawo shi kawai inyaso sai na hanzarta nayi mishi tiyata da gaggawa.
RAMATU: Allah ya kiyaye, sai dai idan kafar ka ce ta lalalce! Kai din ne zan yadda KA yankewa kanin nawa kafa? Mtseewwwww
(SUKA BUSHE DA DARIYA, AKA SAKI SAUTI HAR WAJEN YA SHUDE.
KARSHE.................
KASHI NA UKU
FITOWA TA FARKO: CIKIN KASUWAR UNGUWAR DAWAKI, WAJE, SAFE.SOUND: SAUTIN HAYANIYA DA CINIKAYYAR JAMA'A ACIKIN KASUWA.
YA’U MAI MAGANI: A sai magani, na ciwon kai, ko ciwon baya, ko ciwon kafa, ko ciwon ido, ko ciwon kirji, ko ciwon mara, a sai magani.
Akwai maganin kanjamau, da na daji, da na kwantar da ciki ma a kwai, a sai magani.
Alhaji a miko mkaa na bassir ne?
Hajiya naga idon ki yana hawaye-hawaye, a kawo miki eye tablets ne?
SOUND: SAUTIN KUKAN MASHIN DIN ADAIDAITA SAHU.
IDI: Kai Ya’u, yaya dai?
YA’U MAI MAGANI: Gwaska Idi, lafiya, yaya aikin?
IDI: To yaaaa ne, hado min as usual mana.
YA’U MAI MAGANI: An gama, gwaska, na dari bakwai ko?
IDI: Yau sai a silow, hado na dari biyar kawai, naga yaa ne, kaga ne ai
YAU MAI MAGANI: Ba komai gwaska, ai ana tare gasu nan an hada.
SOUND: SAUTIN KARBAR MAGANI, KIRGA KUDI, DA RURIN TAFIYAR MASHIN DIN ADAIDAITA SAHU.
IDI: Na gode nawan, zamu hade
YAU MAI MAGANI: Ahaa
A sai magani, a saya….maganin basir, maganin shawara, tablet din ido a saya.
MATA 1: Mai magani, yauwa zo, don Allah bani magungunan nan. Daman anjima nake son naje wurin Dr Bala na siya, amma tun da na ganka, shikenan kawai.
(TA MIKA MASA TAKARDAR MAGUNGUNAN DA RAMATU TA RUBUTA MATA)
YA’U MAI MAGANI: Haba! Waye Dr Bala? Wanda shi kansa a gurina yake sayen magani, karki samu damuwa, ai ni kowanne magani kike bukata ina da shi.
(YA KARBI TAKARDAR YA DUBA YA KASA KARANTA KOMAI DON DAMA BAI IYA BA SAI YACE). Tirkashi wadannan magunan na naki babu wanda bani da shi. Amma sai dai fa, akwai tsadar bala’e bare na ukun nan.
MATA 1: Toh, fa! Nawa ne magungunan ne?
YAU MAI MAGANI: Wallahi dai, kin ga wannan, tutolin din nan, dari biyar ne, ga wani chloroquine nan, shi dubu biyu ne, sai kuma na kasan nan, butasolodene, shi ma dubu biyu ne, kin ga dubu hudu da dari biyar kenan.
MATA 1: Anya wadannan sune magungunan kuwa?
YAU MAI MAGANI: Ke! don Allah kar ki raina min wayo mana, ban san su bane? Sune mana. Shekaruna biyar kenan fa ina siyar da magunguna, babu abin da za ki gayamin da ban sani ba.
MAMAN AMINA: Toh shikenan, yi hakuri, miko min su.
SOUND: SAUTIN JARIRIYA NA KUKA.
MATA 1: Yi hakuri, ga magani na siya miki, bari muje kasuwa sai na baki ki sha kin ji ko? Ki yi hakuri.
Yauwa Mai Magani, Allah ya sa magungunan nan na ka na kwarai ne.
YA’U MAI MAGANI: Haba Anty na, kar ki ji komai, wannan Maganin “conpam”ne!
FITOWA TA BIYU: TEBURIN ABINCHIN SU FATIMA, CIKIN KASUWA, WAJE, SAFE.
SOUND: SAUTIN KARAR KWANUKAN ABINCI DA KUMA MAGANGANUN MASU SAYA.
AUDU: Yauwa Fatima, don Allah bani tuwon nan
FATIMA: Tuwon nawa za’a baka?
AUDU: Kawo na dari biyu da nama.
FATIMA: Ruwan famfo ko fuyo wata?
AUDU Ke! Wai yau ina maman ki ne? Ita ta saba hadamin, kin cika mun kunnuwa da tambaya. Hado min komai da komai na dari biyu kawai hahahah
FATIMA: Baba ne yau bai jin dadi, shi yasa yau mama ba ta zo ba. Shikenan, ga tuwon nan za’a kawo maka.
AUDU: Ayyah, Allah ya bashi lafiya.
SOUND: SAUTIN KUKAN JARIRIYA.
(MATA 1 CE TA KARASO WAJEN ABINCIN SU FATIMA GOYE DA JARIRIYAR TA MAI KUKA)
FATIMA: Haba don Allah Maman Amina, sai yanzu za ki zo wurin aiki, haba! Ko dan kinga saboda mama ba ta nan ne?
MATA 1: Yi hakuri Fati, wallahi ba haka bane, Amina ce bata ji dadi ba, sai da na kai ta gurin Ramatu Nas a can karamin asibiti, dawo wan mu kenan. Yau Hajiya ba ta zo bane?
FATIMA: Ayyah, wallahi ban sani ba, ashe shi ya sa na ji shiru. Eh wallahi, Baba ne bai dan jin dadi ba, ta zauna a gida yau.
AUDU: (CIKIN FADA FADA) Wai ina abincin ne?
FATIMA: Yi hakuri, gashi nan za’a kawo maka, Ungo, maman Amina, don Allah karbi ki mika ma sa.
AUDU: Mutum da kudin sa, sai ma anyi mar yanga, toh wallahi gobe ba zan dawo nan ba, haba ban san wulakanci.
MATA 1: Yi hakuri Malam Audu, ni take yiwa magana, shi ya sa.
AUDU: Ba komai Maman Amina, yaya jikin Aminan yanzu?
MATA 1: Da sauki.
AUDU: Toh, Allah Ubangiji ya bata lafiya
FATIMA: Toh, wai mai nene ainihin abin da ke damun Aminan ne?
MATA 1: Wallahi, ji na ke kamar hakori ne, jikin ta zafi, kuma tana zawo.
FATIMA: lalle kam, ba mamaki hakori ne, Amma wane irin magunguna a ka rubuta mata?
MATA 1: Ga takardan nan, wanda Ramatu Nas ta rubuta min, kuma gasu nan ma na siyo a gurin mai tallan magunguna.
FATIMA: Babbar magana, wace nas din ce ta rubuto wa Amina wadannan magungunan? Kuma wani mai tallen maganin yace miki su ne wadannan?
MATA 1: Wallahi Ramatu Nas ce, kuma a gurin Ya’u mai tallan magani na siye su yanzun nan kuwa.
FATIMA: Toh, bari na gaya miki gaskiyar magana, in har kina san ran yarinyan nan, kar ki kuskura ki bata wadannan magungunan nan, saboda na daya maganin da Nas ta rubuta miki basu da alaka da rashin lafiyar dake damun Amina, na biyu magungunan da Ya’u mai Kwaya ya siyar miki, ba ma abin da ke cikin takadar maganin bane.
MATA 1: Innalillahi wa inna illaihir raji’un, wai wai, kuma fa sai da na tambaye ta, har ta fara mun fada, wai kaza da kaza, tayi shekaru a cikin aikin nan, ta san mai ta ke yi, waya mutu - waya tashi.
FATIMA: Saurara ki ji, toh wallahi bari na gaya maki abi na uku, duk magungunan nan da ki ka siya, duk sunyi expire!
SOUND: SAUTIN MATA 1 TA RINGA TAFA HANU TANA SALLALLAMI HAR WAJEN YA SHUDE.
KARSHE...............
KASHI NA HUDU
FITOWA TA FARKO, WAJE RANA.
FATIMA: Malam idi tafiya ne, tafiya ne?
IDI: tafiya ne, ina za'a kai ki? Ko gida zakije ne?
FATIMA: eh wallahi, yanzuma maman Amina ta tafi gida, Yau mun dan yi yamma gaskiya.
IDI: to jau muje Na ajiyeki
FATIMA: yauwa nagode Malam idi.
( IDI YA KASA KUNNA BABUR MAI KAFA UKUN SAKAMAKON RASHIN KARFI DA MAGAGI)
FATIMA: Wai tsaya tukun, Malam idi Yau lafiya kuwa, Naga kamar bakada nutsuwa Yau sosai?
IDI: Yarinya kwantarda hankalinki, shekaru biyar kenan ina wannan aikin, ba abinda zaki gaya min kin zauna sosa? toh, muje
SAUTI: (KARAR KARON BABUR MAI KAFA UKU, FATIMA TA KURMA IHU)
FATIMA: wayyo, kaina, kafata, innalillahi, haba Malam idi, meye haka, kodai Yau a Maye kake ne?
IDI: Don Allaah karki raina min hankali mana, Kai 'yar wannan faduwar zaki Fara min maganganu, dalla tafi can, kuma laifinkine, kece baki zauna sosai ba.
FATIMA: Da Na karye fa, Allaah dai ya sauwake.
IDI: ke, anfasa tafiyar ma kije da kafa
FATIMA: dama, ai bazan kuma binkaba, sabida bansan abinda kasha ba Yau gaskiya.
SAUTI: KARAR DAWOWAR WANI BABUR DIN MAI KAFA UKU DA BAYA.
AUDU: (YACEWA FATIMA) lafiya kuwa fatima, ya naganki duk Kura, ko wani Abu ya farune?
FATIMA: Mallam Audu, wallahi idi ne ya kadani a Babur, Daga yakaini gida, Sai gungura kasa da mu, adaidaita sahun ya kife a kasa, wallahi abun mamaki, kamar ba shi ba.
AUDU: La la la, Ashe ke bakida labari fatima, ai Idi yanzu yafara shaye-shaye, ki godewa Allaah da bai yadda ke a cikin kwata ba, kuma kafarki bata karye ba.
FATIMA: haba Dan Allaah, nima abin yabani mamaki ba kadan ba, Wai, yaushe Idi yazama haka, gashi matarsa tana da hankali sasai.
AUDU: Toh! wallahi, nakirashi, Na Mai magana, duk tabi iska ko ajikinsa.
FATIMA: gashi Naga duk bakinsa ya Fara lalacewa, Ashe shaye-shaye yake, Wai! Allah ya sawwake.
AUDU: Yanzu dai muje Na ajiyeki a gida.
FATIMA: Kawai ka ajiyeni a warin Dr Bala, ya duba mini kafar nan, na dan bugu sanda muka fadi yanzu. Daga nan, kawai Sai Na karasa gida da KAFA.
AUDU: To Bismillah
SAUTI: KARAR TAFIYAR BABUR MAI KAFA UKUN SU YAYIN DA SUKA TAFI.
FITOWA TA BIYU: CIKIN CHEMIST DIN DR BALA, RANA.
DR BALA: (CIKIN MURYAR SOYAYYA) Fatima tawa, ai Yau ban San zamu hadu ba, nasha Sai gobe?
FATIMA: wallahi Idi ne ya kadani akan Babur dinsa, Ashe yaje yasha Kwaya ne ban saniba, duk jikinsa rawa yake.
DR BALA: A'uzubillah, Allaah Yasa bai ji miki ciwo ba.
FATIMA: Ai shiyasa nazo ai, kadan duba min ciwon nan, kasa min koda GV ne da plaster.
DR BALA: Amma Idin nan baida hankali, Rabin ran tawa zai karyawa kafa? Allaah Ya isa wallahi.
FATIMA: (UHM TAYI MURMUSHI) Wai Rabin ransa, Ni fa haryanzu ban yarda dakai ba. irin ku haka, zaku ringa yiwa Mata karya.
DR BALA: haba fatima, nifa nasha an wuce zancen nan, wallahi sanki nake, kuma aure nakeso, tun yaushe nace miki, ki bani damar kawo gaisuwa gidanku, kullum Sai kice ba yanzu ba, kuma gashi lokaci Na ta tafiya.
FATIMA: Toh Bala, naji maganar ka, zanwa babata magana kuma, kasan dai shi Baba, Sai a hankali, baya ma son yaji maganar aure yanzu tunda kaga ban Gama karatu ba.
DR BALA: Shike nan, Allaah yakaimu, nifa Fati, in ba keba Sai rijiya kawai.
FATIMA: (UHM TAYI MURMUSHI) BALA nawa kenan.
DR BALA: Ga shi, nayi miki gyaran ciwon, ga kuma paracetamol kisha in kika je gida. Bari nazo na raka ki.
FATIMA: Kada ka damu, bari nayi sauri, na dan makara, mama zata fara damuwa ban dawo dawuri ba, zamu hadu gobe, insha Allaah.
DR BALA: Allaah Ya tashe mu lafiya masoyiyata.
FITOWA TA UKU: CIKIN GIDAN MAI UNGUWA, DAKIN HAJIA MAIMUNA, RANA.
SAUTI: (BUDE KOFA DA KULLEWA)
FATIMA: Sannu da gida mama
HAJIYA MAIMUNA: Fatima, sannu da dawowa, ya kasuwa?
FATIMA: Kasuwa lafiya mama, mun godewa Allaah
HAJIYA MAIMUNA: amma fa kin Dan Dade, lafiya dai ko?
FATIMA: Wallahi mama, matsala aka Dan samu
HAJIYA MAIMUNA: Matsala? Me yafaru fatima?
FATIMA: Wallahi, na taso daga shago kenan, Sai Na hadu da Malam Idi, yace zai kawo Ni gida.
HAJIYA MAIMUNA: Wane idi kenan?
FATIMA: Idi dai mai adaidaita sahu, Mijin Mai mana wanke-wanke.
HAJIYA MAIMUNA: Toh, Toh, nagane shi, Sai akayi yaya?
FATIMA: Wallahi ina zaune kenan, Sai gamu a kasa, har Na danji ciwo a kafa. Yayi fushi yatafi, Wai duk laifi nane, Sai ga Malam audu yazo wucewa yaganni jikina duk Kura, ai shine yazo yake gayamin cewa Idi ya fara shaye-shaye.
HAJIYA MAIMUNA: A'uzubillah, bakiji ciwo ba dai ko?
FATIMA: Na Dan buge kafa, amma malam Audu ya kaini wajen Dr Bala, ya Dan gyara min ciwo kuma yabani magani. Bakomai mama.
HAJIYA MAIMUNA: Toh mun godewa Allaah, Allaah yaci gaba da karemu, sannu fatima, Allaah yayi miki albarka.
FATIMA: Amin mama, ya jikin Baba, ya danji sauki kuwa?
HAJIYA MAIMUNA: Toh, ba laifi, ya Dan samu yayi bacci, yanzu ma bai tashi ba, Daga dakinsa nake.
FATIMA: Toh, Allaah yabashi lafiya, amma fa yakamata a Kai shi asibitin cikin gari a duba meke damunshi.
HAJIYA MAIMUNA: Ba wani Abu bane, kawai ciwon hakori ne, kuma ya ragu, amma gobe zamuje cibiyar lafiya dashi, muje muga Dr Bala ko Ramatu ma'akaciyar lafiya.
FATIMA: Yauwa ya fi, Allaah yakaimu gobe, amma fa mama ban yarda da Ramatu ma'akaciyar lafiya ba, Sai dai Dr Bala, sabida maman Amina ta je can wurinsu aka hado Mata wasu irin magunguna Wai maganin hakorin yarinyarta ne, kuma wallahi mama duk basu da alaka da abinda yake damunta.
HAJIYA MAIMUNA: Toh! A'uzubillah, shike nan, Sai muje wurin Dr Bala din gobe kenan
FATIMA: Mama, akwai wata maganar fa
HAJIYA MAIMUNA: Maganar me kenan? Lafiya?
FATIMA: lafiya kalau, mama maganar aure ce, Kin tuna nace Dr Bala yace yana sona da aure, kuma har yanzu bakiyiwa baba magana ba.
HAJIYA MAIMUNA: Wai, har gabana yafadi, fatima, kin San babanki bazai bari kiyi aure ba, Sai kin Gama jami'a, duka duka ba shekara daya ya rage ba? Kiyi hakuri, in kika gama, Sai a Fara zancen auren Ko ba haka ba?
FATIMA: (CIKIN DAN KUKAN SHAGWABA) Ni mama, gaskiya bazan jira ba, ayi min aure kawai, in yaje yasamo wata fa, ai Ni nayi asara kenan.
HAJIYA MAIMUNA: Ba wani maganar asara a nan, indai Allaah ya nufi shine mijinki, Babu abinda zai hana.
SAUTI: (FATIMA TA TASHI A FUSACE TABAR DAKIN)
HAJIYA MAIMUNA: Hmmmm, fatima kenan, yarinya bata gane bane, matar mutum kabarinsa, kuma ba Wanda zai auri matar wani, Sai dai tashi, hakuri Fatimatu, hakuri za kiyi.
KARSHE.......
KASHI NA BIYAR:
FITOWA TA DAYA: GABAN ASIBITIN SHA KA TAFI, WAJE, RANA.
SAUTI: (MARASA LAFIYA SUNA TATTAUNAWA A GABAN CIBIYAR LAFIYA YAYINDA DR BALA YAKESHIGOWA)
DR BALA: Barkan ku da asuba, an tashi lafiya? Dan Allaah inaso Mata su zauna a kujerar gaba, maza kuma a kujerar baya, idan Na kirawo Mai shigowa Na gaba inason namiji da farko Sannan mace. Dafatan kowa ya fahimta?
MARASA LAFIYA: (CIKIN HAYANIYA) Eh mun gane.
DR BALA: Toh namiji daya, Bismillah.
SAUTI: (MACE TASHIGO CIKIN CIBIYAR LAFIYAR TANA LA'ANTAR DR CIKIN DAGA MURYA)
MACE 1: Ku masu sanadin mutuwar mutane, ina wannan mayyar Mai kiran kanta malamar lafiya da kuma likita a lokaci daya, muguwar mace, kina ina? Fito yanzu Na tona miki asiri a idon duniya.
DR BALA: Ki kwantar da hankalin ki malama, shigo ciki Dan Allaah ki sanar dani Matsalar
MACE 1: Naki nashigo cikin? Wane irin ciki? Cikin da nashiga aka rubuta mini maganin banza a matsayin maganin cutar 'yata? Wannan matar da tayi rubutun tafito ko kuma Na kona wannan wajen.
MARA LAFIYA1: Malama, ki kwantarda da hankalinki, ki saurari likita.
MARA LAFIYA 2 : Haba hajiya kada ki kona wannan wajen mana, wannan itace cibiyar lafiyar da take Kula da kauyuka biyu, idan kika kona, ina zamuje idan bamuda lafiya?
MARA LAFIYA 3 : Balle, a ina zaki samu man da zaki kona wannan katafaren gurin, malama kiyi hakuri, ko menene Matsalar, kishiga kuyi magana da likita.
Mace 1: Dan Allaah, Wai Ku da kuke cewa nayi hakuri, kunsan wadannan mutanen sun kusa sanyawa na rasa 'yata. Kunsan haka? A takaice banida alaka daku, Kai tsaye gidan Mai unguwa zanje.
DR BALA: Ah, malama, Dan Allaah, shigo muyi magana, shigo mu sasanta cikin sulhu.
MACE 1: Nazo nan da wannan yariyar jiya, kalleta ko shekara bata karasa ba, tana zazzabine da ciwon hakori, amma kalli maganin da ta rubuta mini, duba wannan, wannan wanne irin maganin banza ne?
DR BALA: Malama kiyi hakuri, Na tabbata wannan malamar lafiyar tayi kuskure, ina Mai baki hakuri a madadin ta, bari Na duba yarinyar na rubuta Mata wani maganin
MACE 1: To, gata nan.
DR BALA: Bakomai malama, hakane, yarinyar tana Dan yin zazzabi, Sannan ciwon hakorin sabida bullowar hakorinne, Babu wani Abu da zamuyi akan haka, amma idan kin fita, zaki siya mata paracetamol Na ruwa, akwai mai shagon magani a kan hanya.
MACE1: Wane Mai shagon maganin? Kana nufin Ya'u Mai magani? Mutumin banzar da ya bani wannan magunguna da aka rubuta? Babu yadda zan koma shagon wannan Dan kwayar, kuma koda zan koma, Sai dai naje Na gayamasa Mai unguwa yana nemansa ruwa a jallo.
DR BALA: Haba dai, malama kada ki damu, zan binciki matsalar, Babu bukatar ki sanar da Mai unguwa, ko ki koma wajen Yau Mai magani. Zan tattauna dashi, atakaice nawa kika bashi kudin maganin, zan biyaki kudin.
MACE 1: Dubu hudu da dari biyar.
SAUTI: (DR BALA YA KIRGA WASU KUDADE YA BATA)
DR BALA: Ga kudin nan, Dan Allaah ki tabbatar duk abinda yafaru, sirrine tsakaninmu kada yafita waje. Amma ina zuwa, ina tunanin inada paracetamol Na ruwa a jakata, bari Na duba.
SAUTI: (BINCIKEN JAKA DON NEMAN MAGANIN)
DR BALA: Yauwa, gashinan, don Allaah ayi hakuri
MACE 1: Bakomai likita, ya wuce, nagode sosai, ta juya ta fice.
SAUTI: (BUDE KOFA DA KULLE KOFA)
DR BALA: Kai kai, turkashi, wannan matar tanaso ta lalata mana kasuwancin mu, haba, wane ne zai rubutawa jariri wannan maganin? A'uzubillahi, shima wannan sakaran Ya'un yanzu haka kwayoyi yasha yabugu, duk Sai ransu ya baci.
Mutum nagaba yashigo!!!
MARA LAFIYA 1: Barka da asuba likita
DR BALA: Barka kadai, meyake damunka?
MARA LAFIYA 1: Likita, abinda yake faruwa likita, dasashi Na ne yake zubar da jini, duk lokacin da Na tofar da miyau, Sai ya fito tare da jini, abun yana bani kunya musamman idan Na goge bakina da burushi da sassafe.
DR BALA: Ah, nasan me yake damunki Ana kiran cutar "dental conjunctivitis sclerosis" Sannan gaskiya maganinta yanada tsada sosai, idan har ba cire hakorin za'ayi ba. Matso kusa, Na duba.
MARA LAFIYA 1: Ah, Cire hakori? Dan Allaah ka taimakeni likita, banaso a cire mini hakori, ka taimakeni likita.
DR BALA: Gaskiya malam ina ganin ka fiye ciye ciye da yawa, kuma bai kamata ka dinga cin abinci fiye da biyu ba a rana, kuma gaskiya ya kamata ka dinga samun koda man goge baki ne ka dinga wanke wa ko sau daya be a rana.
MARA LAFIYA 1: Haba Dr na fiya yawan cin abinci kuma? To dai yanzu ya za'a yi mu dakatar da wannan zubar jinin, kga yanzu ma zuba yake, gaskiya akwai matsala.
DR BALA: To, yanzu zaka biya kudin ganin likita, sai na rubuta maka maganin da zaka yi amfani da shi, kayi sa'a a yanzu ba sai an cire hakorin ba, Amma watakila Nan gaba za'a bukaci hakan.
MARA LAFIYA 1: Ah! To alhamdulillahi, nawa ne kudin?
DR BALA: Subu daya be kudin.
MARA LAFIYA 1: To likita ga ta.
DR BALA: To wadan nan zaka saya, zaka biya kudin yanzu, amma sai anjima za ka same ni a kyamis dina.
MARA LAFIYA 1: To bari na biya Mana yanzu, nawa ne kudin maganin kuma?
DR BALA: Naira dubu biyu ne kawai.
MARA LAFIYA 1: To gashi likita, anjima zan zo na karbi maganin a kyamis din, na gode fa.
DR BALA: Ba matsala.
Neeeext!
MARA LAFIYA 2: Dr barka da asubah.
DR BALA: Yawwa barka dai, Hajia Yaya kike?
MARA LAFIYA 2: Gaskiya likita lafiya amma ba Lau ba, kwanaki nazo asibitin nan na yadda Ramatu ma'aikaciyar jinya, gaskiya abinda tamin ban ji dadi ba, nan ta sameni tamin iya wulakancin, kuma ta koren, kuma dama inajin labarin yadda take wulakanta mutane, to Wallahi ni zanyi maganin ta, sai naga bayanta a garin Nan.
DR BALA: Ayyah, kiyi hakuri watakila tana cikin wani yanayi ne, Amma ba haka take.
Yanzu me ke damun ki?
MARA LAFIYA 2: Wallahi likita bana iya cin abinci da barin hagun bakina, dama nasan da akwai rami a turmina na hagun Dan nakan kwakwale ragowar abincin da naci a gun wasu lokutan.
DR BALA: To, zo muga hakorin naki, to bude bakin, Ok na gani, wato kina fama da wata cutacar hakori ce da ake cewa “Rental scabies” kuma gaskiya ana bukatar a cire shi da gaggawa kafin ya harbi sauran hakoran.
MARA LAFIYA 2: A'a, tsaya likita kana nufin babu abinda za'a iya yi sai dai a cire hakorin? Ai ba haka likitan da na gani a birni ya fada min ba cewa yayi za'a iya cike min ramin hakorin a ko Ina kuma ko wane likita, ya Kai zaka ce sai dai a cire babu maganar ciko.
DR BALA: Gaskiya sai dai kiyi hakuri, amma Ramin dake hakorin Nan naki ba wani yashi da simintin da zai cike katon kogon dake hakorin ki gaskiya.
MARA LAFIYA 2: To, naji idan na yadda a cire, za'a iya cire shi yanzu?
DR BALA: Kwarai ma kuwa, ko yanzu kike so sai na cire miki, tunda da kayan aikina a kusa, ko kuma zaki sameni a nawa asibitina ne?
MARA LAFIYA 2: Asibiti? To!? Kana da asibiti ne? A Ina yake?
DR BALA: Kwarai kuwa, Yana karshen titin nan, dab da bakin kasuwa, zaki ga an kafa katon allo, an rubuta ASIBITIN DR BALA.
MARA LAFIYA 2: To nan da kwana biyu zanzo a cire min shi.
DR BALA: To hajiya zan jira ki.
SAUTI: AKA JIYO KARAR BUDEWA DA RUFE KOFA A YAYIN DA MARAR LAFIYAR KE FITA
DR BALA: Tofa! Lallai ya kamata nayi takatsantsan da matar nan naga alamar so take ta bata mana ruwa, Amma wace ita? Nifa bansan ta ba, Amma kamar ita ta sammu ba sanin shanu ba, ba komai zanyi bincike na akan ta, kuma na tabbatar bata, bata Mana abincin mu ba a harkar Nan.
Neeeeeext!!!
KARSHE.......
More
Less
Experience
Years of experience: 17. Registered at ProZ.com: Feb 2020.